30 Yuni 2026 - 17:56
Source: ABNA24
Amurka A Kudancin Lebanon Shirin Jibge Sojojin Sa Ido A Iyakokin Lebanon Da Isra'ila

A bayanan jaridar Washington Post, Amurka tana da niyyar ajiye sojojin sa ido a kudancin Lebanon, don sa ido kan aiwatar da yarjejeniyar tsarin tsakanin Lebanon da gwamnatin yahudawa. Wannan mataki, tare da kawo ƙarshen aikin sojojin UNIFIL da shirye-shiryen Turai don ƙirƙirar aikin sa ido, yana nuna sabon rawar Washington za ta taka a ma'auni na kudancin Lebanon.

Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (AS) – ABNA - ya bayar da rahoton cewa: A yayin da ake ci gaba da cece-kuce da rarrabuwar kawuna a cikin Lebanon game da yarjejeniyar tsarin da aka sanya hannu da gwamnatin yahudawa, bayanan jaridu sun nuna aniyar Amurka na ajiye sojojinta a kudancin Lebanon don sa ido kan yadda sojojin Lebanon da Isra'ila zasu aiawatar da wannan yarjejeniya.

Wani jami'in Amurka wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya shaida wa jaridar Washington Post cewa Amurka za ta taka rawa kai tsaye wajen sa ido kan motsin sojojin Lebanon da sojojin Isra'ila, wanda ya haɗa da amfani da sojojin Amurka a ƙasar Lebanon da Isra'ila. Wannan jami'in ya kara da cewa Amurka tun daga shekara ta 2024 tana da sojoji a Lebanon waɗanda ke taka rawar sa ido, kuma yanzu za su ɗauki alhakin sa ido kan bangarorin biyu da kuma gano duk wani yunurin keta yarjejeniyar.

Wannan bayyani ya zo ne daidai da ziyarar "Brad Cooper," kwamandan cibiyar tsakiya na Amurka (CENTCOM), zuwa Beirut, wanda shine ziyararsa ta farko tun bayan sanya hannu kan yarjejeniyar tsarin. Bisa ga rahotanni, wannan ziyarar ta faru ne a daidai lokacin da ake nazarin rawar da Amurka ke takawa a kudancin Lebanon.

Ra'ayoyin Masana Game Da Rawar Amurka Da Ake Tsammani

Khalil al-Jamil, masanin soji da dabarun siyasa, yana mai nuni da canjin tsarin kwamitin sa ido daga kasancewar Faransa da UNIFIL zuwa ƙirƙirar sabon kwamiti mai bangarori uku wanda ya haɗa da Amurka, sojojin Lebanon da Isra'ila, ya ce Amurka za ta taka rawar sasanci. Bai yi hasashen rawar soji da yaƙi ga sojojin Amurka ba, ya kuma bayyana ta a matsayin sa ido kawai, kuma ya jaddada cewa bangaren Lebanon ya dogara ga wannan rawar saboda ikon da Amurka ke da shi na matsa wa Isra'ila aganinsa.

Rashid Fayyad, marubuci kuma manazarcin siyasa, yana mai nuni da kawo ƙarshen aikin UNIFIL, ya bayyana kasancewar Amurka a matsayin maye gurbin wadannan sojoji, kuma ya yi magana game da ƙoƙarin da Turai ta yi na samar da sojojin sa ido wanda bai yi nasara ba.

Tawfiq Shuman, manazarcin siyasa, yana mai nuni da tarihin kasancewar sojojin ƙasashe dayawa karkashin jagorancin Amurka a Lebanon bayan harin 1982, ya yi hasashen cewa rawar Amurka ta wuce sa ido kawai, kuma tana da niyyar ba da fakewa daa bayar da kariya ga ta'addancin Isra'ila da rashin aiwatar da janyewarsu. Ya bayyana wannan matakin a matsayin ƙoƙari na samar da kariya ta shari'a da siyasa don ci gaba da kasancewar Isra'ila a ƙasashen Lebanon da aka mamaye.

Yarjejeniyar tsarin da aka sanya hannu a ranar 26 ga Yuni 2026 a Washington karkashin sa idon Amurka, ta fuskanci adawa mai yawa a cikin Lebanon. Naim Qassem, babban sakataren Hizbullah, ya bayyana wannan yarjejeniya a matsayin "ɓatacciya" da "mika wuya ga ikon mallaka." A gefe guda, gwamnatin Lebanon ta yi maraba da shirye-shiryen Turai na ƙirƙirar aikin sa ido, amma yanzu tare da bayyana rawar Amurka kai tsaye, an buɗe sabon hangen nesa a ma'auni na kudancin Lebanon.

…………………………

Your Comment

You are replying to: .
captcha