Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (AS) – ABNA - ya habarta cewa: Hukumar hulda da jama'a ta Dakarun Juyin Musulunci, ta hanyar fitar da wata sanarwa, ta ba da labarin cewa ta kai wa sansanin sojan sama na Ramat David, wanda shi ne mafarin tushen hare-haren da ake kaiwa yankin Dahiyah ta Beirut, hari da makamai masu linzami na ballistic na rundunar sojan sama na Dakarun Juyin Musulunci.
Rubutun sanarwar yazo kamar haka:
بسم الله قاصم الجبارین
قَاتِلُوهُمْ یُعَذِّبْهُمُ اللَّهُ بِأَیْدِیکُمْ وَیُخْزِهِمْ وَیَنْصُرْکُمْ عَلَیْهِمْ وَیَشْفِ صُدُورَ قَوْمٍ مُؤْمِنِینَ
Bismillahi Qasimil Jabbarin
Ku yake su; Allah zai azabtar da su da hannayenku, kuma Ya wulakanta su, kuma Ya taimake ku a kansu, kuma Ya warkar da zukatan wasu muminai.
A mayar da martani ga babban laifin da gwamnatin yahudawa ta yi a kudancin Lebanon da kuma kisan kare dangi da korar al'ummar da aka zalunta na yankunan Sur da Nabatiye da sauran wurare ciki har da yankin Dahiyah a Beirut, an kai wa sansanin sojan sama na Ramat David, wanda ya kasance tushen waɗannan hare-hare, hari da makamai masu linzami na ballistic na rundunar sojan sama na Dakarun Juyin Musulunci.
Yardawar da muka yi da tsagaita wuta a ranar 19 ga Afrilu, ta kasance bisa sharadin dakatar da bude wuta a dukkan fagage ne; amma kamar koyaushe, Amurka da gwamnatin yahudawa ba su kiyaye alkawarinsu ba, sun ci gaba da hare-hare da laifuka a Lebanon, kuma sun keta tsagaita wuta ta hanyar cin zarafi akai-akai ga gabar teku da jiragen ruwan Iran a mashigar Hurmuz, Tekun Oman da Tekun Indiya.
Aikin na daren yau gargadi ne, kuma idan aka sake maimaita cin zarafi, martani zai yi faɗi, kuma zai shafi dukkan manufofin Amurka da yahudawa a yankin.
........................................
Your Comment