3 Yuni 2026 - 07:50
Source: ABNA24
Taliban: Tattaunawar A Fakaice Da Pakistan Na Ci Gaba, Bukatun Islamabad Ba Ma Su Yiwuwa Ba Ne

Gwamnatin riƙon kwarya ta Afghanistan ta ce bayan dakatar da tattaunawar kai tsaye da Pakistan, tuntuɓar a fakaice tana ci gaba, amma saboda "bukatu marasa ma'ana" na Islamabad ba a samu ci gaba ba. Kabul ta jaddada cewa bukatarta ita ce mutunta ikon Afghanistan da kuma dakatar da hare-haren kan iyaka, kuma a lokaci guda tana musanta zargin Pakistan game da kasancewar TTP a cikin ƙasar Afghanistan.

Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (AS) – ABNA - ya habarta cewa: Gwamnatin Taliban ta sanar cewa duk da dakatar da tattaunawar kai tsaye da Pakistan, tattaunawar kaikaice tsakanin Kabul da Islamabad tana ci gaba.

Hamdullah Fitrat, mataimaki mai magana da yawun Taliban, ya ce Kabul ta hanyoyi daban-daban tana ƙoƙarin kiyaye hanyoyin sadarwa a bude kuma "kofofin tattaunawa a bude suke".

Fitrat yayin da yake nuni da cewa taron kai tsaye na ƙarshe da bangarorin biyu suka yi ya gudana ne a birnin Urumchi na kasar Sin, ya kara da cewa tun daga lokacin ba a sake yin tattaunawar fuska da fuska ba.

Ya bayyana dalilin dakatar da ci gaban tattaunawar a matsayin "bukatu maras ma'ana na Pakistan" kuma ya ce bukatar Kabul a bayyane take: mutunta yankin da ikon kasa na Afghanistan da kuma dakatar da "hare-haren da ba su dace ba" kan mutanen wannan ƙasa.

A wani bangare na kalaman nasa, mataimakin mai magana da yawun Taliban ya sake musanta ikirarin Islamabad game da kasancewar ko goyon bayan Kabul ga kungiyoyin da ke dauke da makamai da ke aiki a Pakistan, kuma ya ce babu wata kungiya, ciki har da Tehrik-i-Taliban Pakistan (TTP), da ke aiki a cikin ƙasar Afghanistan.

Ya yi ikirarin cewa cibiyoyin wadannan kungiyoyi suna cikin Pakistan ne, kuma ya bayyana batutuwan da suka shafi Balochistan da ayyukan TTP a matsayin "al'amuran cikin gida na Pakistan".

Wadannan matsayai suna zuwa ne a daidai lokacin da Muhammad Ya'qub Mujahid, mai kula da ma'aikatar tsaro ta Taliban, bayan tafiyarsa ta baya-bayan nan zuwa Moscow da tattaunawar tsaro da jami'an Rasha, ya dauki matsayi mai tsauri kan Pakistan.

Ya fada cewa Pakistan a nan gaba kadan ba za ta "kuskura ta kai harin sama" kan Afghanistan ba, kuma duk wani matakin soja zai fuskanci "martani daidai gwargwado"; matsayin da wasu manazarta ke ganin yana iya kasancewa da alaka da tuntuɓar tsaro tsakanin Kabul da Moscow.

A lokaci guda kuma, majiyoyi da aka sani sun ba da rahoton shirin ci gaba da tuntuɓar da ba ta hukuma ba tsakanin Taliban da Pakistan a Kabul.

An shirya gudanar da wadannan tattaunawar ne kafin Idin babbara Sallah, amma a cewar majiyoyi, wasu kalubale daga Pakistan sun jinkirta ta.

A zagayen farko na wadannan tarurruka, daga Afghanistan Atif Mashal, Ubaidullah Bahir, Ja'afar Mahdawi da Ghanche Gul Arman sun halarta, daga Pakistan kuma Asif Durani, Mushahid Hussain da Hamid Mir suka halarta.

A cikin shekarun baya-bayan nan kuma an gudanar da tattaunawa da dama a Istanbul, Doha da Urumchi, amma ba su kai ga wani sakamako mai amfani ba.

A Doha, yunkurin samar da tsarin tsaro na hadin gwiwa ya tsaya cikas saboda sabani kan yadda za a dakile TTP, kuma a Istanbul ma, sabani kan sa ido kan iyaka da ma'anar barazanar tsaro ya hana cimma yarjejeniya.

Taron ƙarshe na Urumchi an gudanar da shi ne da tsakancin kasar Sin; ko da yake bangarorin biyu sun yi magana game da yanayi mai kyau, amma taron ya ƙare ba tare da wata nasara ta musamman ba, kuma sabani ya ci gaba da wanzuwa.

……………………………………………………..

Your Comment

You are replying to: .
captcha