Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (ABNA) ya ruwaito cewa: A tsakiyar kallafaffen yaƙin da aka kakabawa Iran na kwanaki 40, wani manazarcin Kuwaiti ya yi wani ikirari da ba a taɓa yin irinsa ba, ya ce: "Mun ba wa surukin Trump kuɗi mai yawa, amma duk da haka an yi mana ruwan makamai da bama-bamai. Suna yi mana kamar dukan ƙasashen Larabawa dole ne su sa Isra'ila ta ji daɗi".
Bayan wannan ikirari mai tsauri na manazarcin Kuwaiti, wani jami'in Saudiyya a lokacin yaƙin ya fada wa tashar Al Jazeera: "Amurka ta yi watsi da kare ƙasashen Larabawa na yankin tekun Farisa; ƙasashen da sansanonin sojan Amurka ke a cikinsu, don haka sun zama masu fuskantar hare-haren ramuwa daga Iran… amma karfin tsaron Amurka ya mayar da hankali ne kawai kan gwamnatin Isra'ila".
Duk da irin barnar da Larabawa suka sha a cikin yaƙin kwanaki 40, jaridar New York Times ta ruwaito cewa za su sake bin hanyar da suka taka a baya: "domin Amurka ta amince da siyar da kayayyakin yaƙi na dala biliyan 9.3 ga Kuwait, dala biliyan 6.25 ga UAE, da dala biliyan 1.625 ga Bahrain".

New York Times ta nakalto wasu jami'ai: Washington ta amince da yarjejeniyoyin sayar da dubunnan makamai na kariya ga Kuwait, UAE, da Bahrain wanda darajarsu ta kai dala biliyan 17. A cewar rahoton New York Times, jimillar yarjejeniyoyin sayar da makamai da ma'aikatar harkokin waje ta amince da su ga ƙasashen yankin ranar Juma'a, ta kai dala biliyan 25.7.
Wani mai fafutuka kuma ɗan siyasar Ingila-Falasdinawa a cikin kasashen Larabawa ya ce: "Yayin da Iraniyawa da kansu suke kera makamai iri-iri, mu mun mayar da al'ummominmu masu cin kasuwa da shagaltuwa da nishaɗi, muna jira mu ga abin da za su aiko mana daga waje".
Your Comment