Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (ABNA) ya habarta cewa: Sojojin sun kai hari da jirege marasa matuƙa a tsakanin garin Kafarshuba da Kafrahma da ke kudancin Lebanon a matsayin ci gaba da mamaye yankin Lebanon.
A daya hannun kuma, tashar gwamnatin Sahayoniyya ta Channel 12 ta ruwaito majiyoyin na cewa gwamnatin na cikin shirin ko-ta-kwana a cikin yankunan da aka mamaye da kuma yankin kan iyaka saboda fargabar hare-haren da kungiyar Hizbullah za ta kai na martani. Majiyoyin Ibrananci sun kuma bayar da rahoton cewa, an soke ayyukan jama'a a yankunan da ke kan iyaka da Lebanon saboda yiwuwar kai hare-haren ramuwar gayya na Hizbullah.
Your Comment