16 Disamba 2025 - 09:26
Source: ABNA24
Saudiyya Ta Kai Hari Kan Yankunan Kan Iyakar Yemen

Sakamakon hare-haren, an lalata kadarorin 'yan kasar Yemen kuma an haifar da tsoro da damuwa a tsakanin al'umma.

Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (ABNA) ya kawo maku rahoton cewa: Kafafen yada labarai na Yemen sun ruwaito cewa sojojin Saudiyya sun kai hari kan kauyukan kan iyakar Yemen.

A cewar rahotanni, an kai wadannan hare-haren ne a fili bisa karya dokoki da ka'idoji na kasa da kasa a matsayin ci gaba da hare-haren da gwamnatin Saudiyya ke kai wa yankunan kan iyakar Yemen.

A cewar kafofin yada labarai na Yemen, wannan harin da gwamnatin Saudiyya ta kai kan yankunan kan iyakar Yemen ci gaba ne na hare-haren da Saudiyya ke kai wa ne kowace rana a yankunan kan iyaka. Harin ya zuwa yanzu ya haifar da lalacewar kayayyaki kuma yana barazana ga rayuwar 'yan kasar.

Your Comment

You are replying to: .
captcha