Hedikwatar tsaro a Najeriya tace kungiyar na yin haka ne sakamakon luguden wutar da dakarun Najeriya ke yi wa mabuyar mayakanta.
A cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun kakakin ma’aikatar tsaron Janar Rabe Abubakar ta ce tuni kungiyar Boko Haram ke daukar Matasa ta hanyar ba su rancen kudi a yankin arewa maso gabashi.
Sanarwar tace kungiyar na janyo hankalin masu kananan sana’oi kamar masu sana’ar dinki da mahauta da wasu sana’oin hannu.
Sanarwar tace bayan karbar bashin ana ba mutanen zabi ko dai su shiga kungiyar ko kuma a kashe su idan sun kasa biyan bashin a wa’adin da aka ba su.
Sannan sanarwar ta gargadi mutane su kaucewa karbar rance daga hannun wadanda hukuma ba ta san da zamansu ba.288