9 Janairu 2016 - 16:52
An samu yamutsi a zaben Bayelsa

Rahotanni daga jihar Bayelsa da ke kudancin Najeriya na cewa an samu hargitsi a karamar hukumar Ikeremu, inda wasu bata gari suka yi kokarin sace akwatunan zabe a wasu rumfuna.

Wasu rahotannin ma na cewa ana zargin an kona gidan tsohon mataimakin gwamnan jihar wanda dan jam'iyyar PDP ne.

Sai dai mataimakin shugaban 'yan sanda DIG Salihu Hashimu ARgungu , wanda mai sa ido ne a zaben, ya shaida wa manema labarai cewa babu abin da ya faru kuma komai yana tafiya yadda aka tsara.

An dai fara zaben a kan lokaci a wasu rumfunan amma a wasu wuraren har zuwa karfe biyu na ranar Asabar ba a fara kada kuri'a ba.

Tun da fari Kakakin hukumar zabe ta kasa INEC, Mista Nick Dazan, ya yi wa wakilinmu bbc: karin bayani kan yadda hukumarsu ta shirya don zaben:288