Al-amarin ya faru ne a yankin Agouza da ke cikin birnin yayin da jaridun kasar suka rawaito cewa, wasu mutane uku ne rufe da fuskokinsu suka wurga bam din kafin su bai wa kafarsu iska.
Tun lokacin da sojoji suka kifar da gwamnatin Mohamed Morsi a shekara ta 2013, ‘yan tawaye ke kaddamar da hare hare a Masar amma sun fi kai farmaki akan jami’an tsaron kasar.288