Motocin buldozar gwamnatin haramtacciyar kasar Isra'ila suna ci gaba da lalata gidajen Noor Shams.
Tun da safiyar yau ne motocin buldozar yakin haramtacciyar kasar Isra'ila ke ci gaba da gudanar da ayyukan rusau a sansanin Nur Shams da ke gabashin birnin Tulkarm da ke arewacin gabar yammacin kogin Jordan.
A rana ta 26 da fara kai hare-hare a sansanin Noor Shams da ke gabar yammacin kogin Jordan, gwamnatin Isra'ila ta fara rusa tare da tarwatsa gidajen mutane 50 a sansanin.
Wasu iyalai da ke zaune a wadannan gine-ginen sun yi nasarar komawa gidajensu a daren jiya bisaizinin maharan tare da yunkurin kwashe wasu kayan da daukarsu na tafi da gidanka, amma sai sojojin Isra’ila ba su bari wasu sauran iyalai su yi haka ba kuma suka hana su dawowa ta hanyar yin harbi zuwa gare su, kuma har ma sun tsare wata mata na dan lokaci sannan suka sako ta.
Hamas: Ayyukan rusau ba za su dakatar da boren Falasdinawa a Yammacin Kogin Jordan ba
Daya daga cikin Shugabannin kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas Abdul Rahman Shadid ya jaddada cewa rusa gidaje da tilasta gudun hijira da sojojin gwamnatin sahyoniyawan suke yi a garin Jenin da ke Tulkarm da kuma sansanin Nur Shams zai yi nasara ba wajen tinkarar tirjiyar al'ummar Palastinu kuma ba za ta cimma burinta na kawo karshen gwagwarmaya da kuma kawar da batun 'yan gudun hijira ba.
Shadid ya bayyana a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis cewa: Shirye-shiryen 'yan mamaya da suka tsananta a sansanonin Jenin da Tulkarm kuma za a fadada su zuwa wasu sansanonin da ke gabar yammacin kogin Jordan, na bukatar farkawa da hadin kan al'ummar Palasdinu don tunkarar hadarin da ke tattare da kawar da batun 'yan gudun hijira.
Ya kuma kara da cewa wajibi ne a kara kaimi wajen yakar gwamnatin mamaya da kuma sahayoniya yan share guri zauna a kasar, yana mai cewa bai kamata samu a wani yanki na kasarmu da ya zama wajen aminci ga wadannan ‘yan mamaya ba, kuma a kai musu hari ta ko’ina da kuma tunkarar duk wani hari da ake kai wa yammacin kogin Jordan.
Ya yi gargadin cewa gwamnatin mamaya na da niyyar kawar da batun 'yan gudun hijira gaba daya, tare da sake gina sansanonin Yammacin Kogin Jordan, da yin kaurar dole ga mazaunanta, da hana sake gina sansanonin, da kuma mika mazaunanta zuwa wasu garuruwan Falasdinu domin kwace matsayinsu na 'yan gudun hijira da kuma kawar da tunanin komawa har abada zuwa gidajensu.
Abdul Rahman Shadid ya bayyana cewa ‘yan mamaya sun kasa kawo karshen lamarin Palastinu saboda wayar da kan al’ummarmu, kuma ya bayyana a gare su yadda wannan maganar ta ke cew “dattijai suna mutuwa kuma al’ummai masu zuwa sukan manta da su” ba ta da ma'ana, domin kuwa dattijai sun yi wasiyya da mabudin komawa da gwagwarmaya ga ‘ya’yansu da jikokinsu, kuma wannan tunanin ba zai gushe ba har sai karshen mamaya.
Your Comment