Kamfanin dillancin labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (A.S.) - ABNA- ya habarta maku cewa, a yammacin jiya, yayin ganawarsa da Sheikh Tamim bin Hamad bin Khalifa Al Thani, Sarkin Qatar, da tawagar da ke tare da shi, Ayatullah Khamenei, ya jaddada cewa, fadada alaka da makwabt wata manufar siyasa ce tabbatacciya a tsarin Jamhuriyar Musulunci ta Iran, yana mai cewa: "Daya daga cikin manufofin gwamnatin Jamhuriyar Musulunci ta Iran ita ce fadada alaka da kasashen waje. An yi ayyuka masu kyau a wannan fanni kuma an samu wasu ci gaba, kuma Malam Araqchi, mai girma ministan harkokin wajen kasar, yana da himma da kwazo a wannan fanni".
Jagoran juyin juya halin Musuluncin ya bayyana fatansa na ganin cewa yarjejeniyar da aka cimma a birnin Tehran za ta amfanar da kasashen biyu, kuma bangarorin biyu za su iya aiwatar da ayyukan makwabtaka fiye da da.
A cikin wannan ganawar, Ayatullah Khamenei ya kuma yi ishara da maganganun da Sarkin Katar ya yi kan batutuwan yankin inda ya kara da cewa: Muna daukar kasar Qatar a matsayin abokiyar kasa da 'yan uwantaka, duk da cewa har yanzu akwai wasu batutuwan da ba a fayyace ba, kuma ba a warware su ba, kamar mayar da bukatun Iran da aka aiko su daga Koriya ta Kudu zuwa Qatar, kuma mun san cewa babban abin da ke hana aiwatar da yarjejeniyar da aka cimma a wannan fanni ita ce Amurka.
Ya kara da cewa: "Idan da muna matsayin Qatar, da za mu yi watsi da matsin lamba na Amurka, mu maido da bukatun ɗayan bangaren, kuma muna ci gaba da sa ran daukar irin wannan mataki daga Qatar."
Jagoran juyin juya halin Musulunci ya jaddada cewa: Babu wani bambanci tsakanin shugabannin Amurka.
A wannan taro da ya samu halartar shugaba Pezzekian, Sarkin Qatar Sheikh Tamim bin Hamad bin Khalifa Al Thani ya bayyana jin dadinsa da ganawa da Jagoran juyin juya halin Musulunci tare da jinjinawa irin matsayin da Jamhuriyar Musulunci ta Iran take da shi na tallafawa al'ummar duniya da ake zalunta da kuma al'ummar Palastinu da yake magana ga Jagoran juyin juya halin Musuluncin ya ce: " Jajircewar Mai girma ga al'ummar Palastinu abu ne da ba ba za a taba mantawa shi ba".
Dangane da takamaiman yanayi da mawuyacin hali a yankin, Sarkin Qatar ya yi la'akari da wadannan yanayin da ke bukatar karin hadin gwiwa tsakanin kasashen yankin.
Sheikh Tamim bin Hamad bin Khalifa Al Thani ya kuma yi ishara da yarjejeniyoyin da aka cimma tsakanin Iran da Qatar da suka hada da gina ramin ruwa a karkashin ruwa tsakanin kasashen biyu, ya kuma ce: Bisa yarjejeniyar da aka cimma, za a fara aiki da kwamitin hadin gwiwa na kasashen biyu nan ba da dadewa ba, kuma za a kara ƙarfafa mu'amalar tattalin arziki nan gaba kadan.
