9 Nuwamba 2024 - 19:40
Salon Rayuwar Ahlul Baiti (As) Umarni Da Kyakkawan Aiki Da Tarbiyya A Cikin Iyali A Cikin Rayuwar Imam Muhammad Baqir (A.S.)

Imam Sadik (a.s) ya ce mahaifinsa ya ce game da tsarin tarbiyya: “Babana Imam Muhammad Bakir (a.s.) ya kasance yana tara mu yana bukatarmu mu da mu rika zikirin Allah har zuwa fitowar rana, wadanda ackinmu suke da ikon karanta Alkur'ani sai ya umarce su da su karanta shi, wadanda kuma ba su da damar iya karanta Alkur’ani sai ya ce da su su yi ta zikirin Allah.

Imam Sadik (a.s) ya ce mahaifinsa ya ce game da tsarin tarbiyya: “Babana Imam Muhammad Bakir (a.s.) ya kasance yana tara mu yana bukatarmu mu da mu rika zikirin Allah har zuwa fitowar rana, wadanda ackinmu suke da ikon karanta Alkur'ani sai ya umarce su da su karanta shi, wadanda kuma ba su da damar iya karanta Alkur’ani sai ya ce da su su yi ta zikirin Allah.

 

Ya zo a cikin ayoyi da ruwayoyi cewa abun sone kuma yana da matukar muhimmanci karanta addu’o’i da zikiri bayan sallolin farilla, wadanda wadannan addu’oi ana la’akari da su a matsayin “Ta’aqibar sallah”, wato addu’oi da suke zuwa bayan yin sallah kaitsaye haka nan kuma Allah yana son cewa yayin da idan bawansa ya bi umurninsa ya yi sallah ya roki Allah wani abu da to ya bas hi wannan abun da ya roka. Ana so bayan sallar asuba har rana ta fito, mutum ya shagaltu da yin addu'a da karatun Alqur'ani.

 

Madogara Al-Wasa’ilish Shia, juzu'i na 4, shafi na 1185, ruwaya ta 1.