Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti{A.S} - ABNA : ya nakalto Ra’isi yana fadar gaka a safiyar yau Asabar a lokacinda yake jagorantar kwamitin yaki da cutar Covid 19 na kasa a nan birnin Tehran.
Ra’isi ya kara da cewa, kasar Iran tana cikin wani mummunan halin dangane da cutar ta Covid 19, don haka ya kara yin kira ga sojoji da kuma wasu kungiyoyin sa kai, da su yi iyakar korarinsu don yaki da wannan cutar, tare da bangaren gwamnati.
342/