5 Satumba 2025 - 16:27
Source: ABNA24
An Yi Musayar Wuta A Kan Iyakar Siriya Da Iraki

Majiyoyin cikin gida a Bagadaza sun ruwaito cewa, an yi harbe-harbe daga cikin kasar Syria zuwa ga dakarun Iraki a yankin "Bukamal" kan iyaka da yammacin jiya. Har yanzu dai ba a fayyace dalilin daukar wannan mataki ba kuma babu wata kungiya da ta dauki alhakinsa.

Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na na Ahlul Baiti (AS) – ABNA– ya habarto cewa: Har yanzu jami’an Iraqi ba su mayar da martani a hukumance kan lamarin ba. A baya dai an buga rahotannin karin motsin kungiyoyi masu dauke da makamai a yankunan kan iyakar Siriya da Iraki.

Birnin Bukamal yana gabashin lardin Deir Ezzor na kasar Siriya, kusa da iyakar kasar Iraki. Birnin ya kasance karkashin ikon kungiyar Nusra ne a lokacin yakin basasar Syria a shekara ta 2013 kuma bayan shekara guda ya fada karkashin ikon ISIS.

Tags

Your Comment

You are replying to: .
captcha