25 Agusta 2021 - 10:08
Aljeriya Ta Yanke Alakar Diflomatsiyya Da Morocco

Kasar Aljeriya, ta sanar da yanke alakar diflomatsiyyarta da kasar Morocco, daga yau Talata, kamar yadda ma’aikatar harkokin wajen kasar Alejeriyar ta sanar.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti{A.S} - ABNA : Har zuw alokacin fasara wadanan labaren babu wani karin bayyani kan dalilin daukar wannan matakin daga hukumomin na Algers , saidia sanin kowa ne dangantaka tsakanin kasashen biyu ta yi tsami a baya bayan nan.

Kafin hakan dai Aljeriya ta sanar a kwanan baya cewa, za ta sake duba alakarta da kasar Morocco, bisa zargin Masarautar da hannu a wutar dajin da ta kashe mutane da dama da lalata dukiya a kasar.

Gomman mutane ne ciki har da sojoji suka rasa rayukansu a wutar dajin wacce ta fara ci tun daga ranar 9 ga wata.

A cewar sanarwar fadar shugaban kasar, ayyukan kiyaya da Morocco ke aikatawa kan Aljeriya, su ne suka tilasta kwakware alakar dake tsakanin kasashen biyu da kuma tsaurara matakan bincike na tsaro a iyakokin yamma.

342/