21 Afirilu 2021 - 12:48
Majalisar Riko Kwarya Ta Soja A Kasar Chadi Ta Kaddamar Da Sabbin Mambobinta

Dan mamacin shugaban kasar ta Chadi, Lafatanar Janar Muhammad Idriss Deby Itno, ne ya gabatar da manyan jami’an soja da zai aiki da su domin tabbatar da cewa an mika mulki ga farar hula a cikin watanni 18 masu zuwa.

ABNA24 : Mamabobin majalisar riko kwaryar dai sun kunshi manyan jami’an soja goma sha biyar a karkashin jagoran Laftanar janar Lieutenant General Mahamat Idriss Deby.

Wannan sanarwar dai ta zo ne adaidai lokacin da jam’iyyun siyasa da kuma kungiyoyin fararen hula su ka bukaci a mika mulki ga shugaban majalisar dokoki kamar yadda tsarin mulkin kasar ya tanada.

A jiya ne dai aka sanar da cewa shugaban kasar ta Chadi Idriss Deby ya rasu bayan da ya sami raunkuna a filin dagar fada da ‘yan tawaye.

342/