ABNA24 : Kamfanin dillancin labaran reuters ya nakalto alkalin alkalan kasar mai shari’a David Maraga ya na cewa “duk tare da wanan dokar a halin yanzu mata sune rike da kashi 21% na kujeru a majalisar wakilan kasar, a yayinda suke da kashi 31% a majalisar dattawa, wanda ya nuna cewa yan majalisa maza ne suke rike da fiye da kashi 2/3 na majalisar dokokin kasar a majalisun dokokin guda biyu.
Kashi 1/3 na ma’aikatan gwamnatin miliyon 2.5 a kasar Kenya dai mata ne, sannan mata ne suke samar da kashi 80% na abincin da mutanen kasar suke ci. Amma kuma suna da, kashi 1% kacal na filayen noma a kasar.
Har’ila yau labarin ya kara da cewa wannan hukuncin shawara ce ga shugaban kasar, babu dole ciki, musamman ganin irin halin da kasar take ciki na karancin kudade.
342/