13 Satumba 2020 - 12:03
Syria:Rasha Ta Gargadi Kungiyar ‘Yan Ta’adda Ta Jibhatunnusra Kan Amfani Da Makaman Guba A Lardin Idlib

Ma’aikatar tsaron kasar Rasha ta gargadi kungiyar ‘yan ta’adda ta Jabhatun Nusra kan shirinta na amafani da makaman guba kan mutanen lardin idlib don cimma manufar ta ta zargin gwamnatin kasar syriya da amfani da makaman.

ABNA24 : Kamfanin dillancin labaran SANA na gwamnatin kasar ta Syriya ya nakalto Elexander Grankovich wani babban jami’a a ma’aikatan tsaron kasar ta Rasha yana fadar haka.

Ya kuma kara da cewa “rahotannin sirri da muka samu sun nuna cewa kungiyar ta gayyaci yan jiridu daga kasashen waje zuwa Jabal Zawiya don daukar daukar hotunan hare haren na guba kan mutanen lardin idlib sannan su yi amfani da su don zargin sojojin gwamnatin kasar Syriya da aikta laifin.

Gwamnatin kasar Amurka da kawayenta a yankin kudancin Asia suna tsoron faduwar kungiyoyin ‘yan ta’adda wadanda suka kirkiro a kasar ta Syriya.

342/