16 Yuni 2020 - 08:33
Trump Zai Jenye Wasu Sojojin Amurka Daga Jamus Saboda Rashin Kashewa NATO Kudade

Shugaban kasar Amurka Donal Trump ya ce zai ci gaba da shirinsa na janye sojojin kasar 9,500 daga kasar Jamus saboda kin kashewa kungiyar NATO kudade.

(ABNA24.com) Shugaban kasar Amurka Donal Trump ya ce zai ci gaba da shirinsa na janye sojojin kasar 9,500 daga kasar Jamus saboda kin kashewa kungiyar NATO kudade.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto shugaban yana fadar haka a jiya Litinin. Ya kuma kara da cewa regewar yawan sojojin Amurka karkashin kungiyar tsaro ta NATO a kasar Jamus zai dawo 25,000.

Ba’a sani ba, ko wannan shirin zai tabbata don tuni an ji cewa masu bawa shugaban kasar shawara a cikin jam’iyarsa ta Republican suna sukan matakin da ya dauka. Inda suke ganin yin hakan ya kamar bawa kasar Rasha kyauta.

Kafin haka dai, a shekara ta 2014 kasashen kungiyar tsaro na ta NATO 30, sun amince su kashe kashi 2% na kudaden da suke samu a shekara, a bangaren tsaro, amma da dama basu yi haka ba, daga ciki har da kasar Jamus.



/129