Kamfanin dillancin labaran shafin sadarwa na yanar gizo na Ahlul-Baiti (A.S) - ABNA - ya habarta cewa, Ayatullah Reza Ramezani a tafiyar kasar Kenya ya samu tarbar Dr. Ja'afar Barmaky jakadan jamhuriyar musulunci ta Iran a birnin Nairobi tare da wasu gungu na masu kula da al'adu da addini na wannan kasa.
Har ila yau Babban Sakatare Janar na Majalisar Ahlul-Baiti (AS) ya jaddada wajabcin kara mu'amalar kimiyya da al'adu tsakanin Iran da Kenya a yayin halartarsa ofishin jakadancin Iran da ke Nairobi.
Dangane da karatun wasu matasa 'yan kasar Kenya da suke yi a jami'ar Jamia Al-Mustafa da ke birnin Qom, Dakta Barmaki ya ce: ita ma Jami'ar Ahlul-Baiti za ta iya ba wa daliban Afirka kaso mai tsoka tare da yin amfani da damar da ake da su a Kenya don gabatar da kansu.
Ya kamata a lura da cewa Ayatullah Ramezani a ci gaba da shirye-shiryensa a ziyarar da ya kai kasar Kenya, baya ga ganawa da masana al'adu da addini, ya ziyarci wasu cibiyoyin addini na kasar, inda ya halarci taron mai taken "Musulmi Matasa: Imani, Kimiyya, Fasaha da makomar Afirka".

