Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : ابنا
Laraba

13 Satumba 2023

11:39:45
1393359

Ayatullah Jannati: Jakadun Tattakin Arbaeen Ya Kamata Su Aza Harsashin inganta Ruhi A Cikin Al'umma

Akwai Bukatar Tunkarar Shiri Da Dabarun Tsare-tsare Na Makiya

Kamfanin dillancin labaran shafin sadarwa na yanar gizo na Ahlul-Baiti (A.S) - ABNA - ya habarta cewa, Ayatullah Jannati yayinda yake jawabi a wajen taron Shugabannin majalisar kwararrun jagoranci ya fuskantar da bayaninsa ga wadanda suka halarci wannan taro na Arbaeen da cewa: Ku dauki kanku a matsayin jakadun Arbaeen kuma ku kula tare da kuma kare ilimi da ruhiyya da aka samu daga wannan taro na addini domin ku zama tushen daukaka matsayin ruhi a cikin al'umma.

Yayi kira da ga masu Fahasa da Yada Labarai inda ya ce : Masu fasahar al'adu da kafofin yada labarai na juyin juya hali su ma su tsara yadda za su tunkari shurun ​​kafafen yada labarai na duniya masu mulki dangane da wannan lamari mai girma da kuma daukarsa a matsayin misali na jihadi.

Shugaban majalisar kwararrun jagoranci yayi tsokaci dangane da ganawar da al'ummar lardin Sistan da Baluchistan da kuma kudancin Khorasan suka yi da Jagoran ya bayyana cewa: A cikin wannan ganawar, Jagora ya gabatar da cikakken bayani dalla-dalla kan tsare-tsaren makiya, wanda ya wajaba masu goyon bayan juyin juya halin Musulunci da su yi taka tsantsan a cikin wannan cikakken bincike, su san kuma me ya hau kansu wanda ya kamata su aikata wajen tunkarar dabarun makiya da tsare-tsarensu don su magance su.