Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : ابنا
Talata

23 Mayu 2023

07:11:25
1367915

Iran: Gwamnatin Jamus Ce Ke Da Alhakin Baiwa Gwamnatin Saddam Makamai Masu Guba

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar ya bayyana cewa: Gwamnati karkashin ministan harkokin wajen Jamus ita ce ke da alhakin baiwa gwamnatin Saddam makamai masu guba tare da kashe dubban 'yan kasar Iran da guba.

Kamfanin dillancin labaran shafin sadarwa na yanar gizo na Ahlul-Baiti (A.S) - ABNA - ya habarta cewa,

"Nasir Kanaani" ya rubuta a shafinsa na Twitter cewa: "Da wuya ministan harkokin wajen Jamus bai san tunanin al'ummar Iran game da iskar gas da sinadarai da alakarta da gwamnatin Jamus ba."

Kanaani ya yi ishara da cewa gwamnatin Saddam na da makamai masu guba, ya kuma jaddada cewa: Ta yaya shi wanda gwamnatinsa ke da alhakin baiwa gwamnatin Saddam makamai masu guba da kuma kashe dubban 'yan kasar Iran guba, ya bai wa kansa damar yin magana kan lamarin hakkin bil'adama na al'ummar Iran!