Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : ابنا
Litinin

22 Mayu 2023

08:45:14
1367744

Kasar Kenya Na Maraba Da Ci Gaban Hadin Gwiwar Al'adu Da Addini Da Iran

Muhammad Reza Khatibi, shugaban cibiyar tuntubar al'adun kasar Iran a kasar Kenya, da Abuzar Odhiambo Ngang A, sakataren al'ummar musulmi na Ambuga a birnin Hamabai, sun gana, inda suka tattauna hanyoyin yada koyarwar kur'ani a kasar.

Kamfanin dillancin labaran shafin sadarwa na yanar gizo na Ahlul-Baiti (A.S) - ABNA - ya habarta cewa, Abuzar Odhiambo Ngang'a, a matsayin wakilin 'yan uwa musulmi mabiya mazhabar shi'a na birnin Ombuga a birnin Hamabai, ya jaddada wajabcin jagorantar al'umma da ilmantar da yara a makarantu ta hanyar koyar da darussa na ilimin kur'ani.


Yayin da yake bayyana irin dimbin karfin da kasashen Kenya da Iran suke da shi na karfafa alaka a tsakaninsu, ya ce: Muna son bunkasa hadin gwiwar al'adu da addini da Iran.