Kamfanin dillancin labaran shafin sadarwa na yanar gizo na Ahlul-Baiti (A.S) - ABNA - ya habarta cewa, Abuzar Odhiambo Ngang'a, a matsayin wakilin 'yan uwa musulmi mabiya mazhabar shi'a na birnin Ombuga a birnin Hamabai, ya jaddada wajabcin jagorantar al'umma da ilmantar da yara a makarantu ta hanyar koyar da darussa na ilimin kur'ani.
Yayin da yake bayyana irin dimbin karfin da kasashen Kenya da Iran suke da shi na karfafa alaka a tsakaninsu, ya ce: Muna son bunkasa hadin gwiwar al'adu da addini da Iran.