Hakan dai zai bashi damar ci gaba da shugabancin kasar na tsawon wa’adin mulki na shekaru 7, masu zuwa.
Shugaban majalisar dokokin kasar Hamoudeh Sabbagh, ya ce Bashar al-Assad ya lashe zaben ne da kaso 95.1 na kuri’un da aka kada, sabanin kuri’u kaso 88.7 na shekarar 2014.
A ranar 17 ga watan Yulin 2000 ne shugaba Assad ya maye gurbin mahaifinsa Hafez al-Assad a matsayin shugaban kasa.
Karkashin kundin tsarin mulkin kasar na 2012, shugaban kasa na da damar tsayawa takara sau biyu, wanda ke nufin, wannan ne wa’adin shugaba Assad na karshe.
342/
