Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : hausatv
Alhamis

6 Mayu 2021

13:56:09
1138368

​Babban Kwamandan Dakarun IRGC Ya Ce Mai Yiyuwa Bugu Daya Ga Isara’ila Ya Isa Ya Kawo Karshenta

Babban kwamandan dakarun kare juyin juya halin musulunci a nan Iran Manjo Janar Husain Samami ya bayyana cewa mai yuwa duka daya zata gama da haramtacciyar kasar Isra’ila ganin irin mummunan halin da ta shiga ciki a fagage da dama.

Salami ya bayyana haka ne a wata harin da yayi da wata tashar talabijin a nan Tehran. Ya kuma kara da cewa, a bangaren tsaro boma-boma da facewa iri-iri na ta aukuawa a cikin kasar ba tare da gwamnatin ta bayyana dalilan aukuwarsu ba.

Daga cikin fashe-fashen dai akwai na tashar Jiragen sama na Bengerion, da ta kamfanin kirar makamai da kuma wadanda suke shafi jiragen ruwa a cikin ‘yan watannin da suka gabata. Har’ila yau ga fashewa ta Haifa da kuma kama jami’am Mosad a kasar Iraki da sauransu.

A bangaren siyasa kuma Janar Salami ya bayyana cewa bayan zabe har guda 4 ‘yan siyasar HKI sun kasa kafa gwamnatin wanda ya nuna babu wata nutsuwa a harkokin zamantakewa a kasar.

Ya ce a wasu wuare farin haramtacciyar kasar bai fi kilomita 14 kacal ba.

342/