Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (AS) – ABNA - ya habarta cewa: Jaridar Saudiyya "Ar-Riyadh" - kafar yada labarai ta hukumar Saudiyya - a cikin wani rahoto da ta yi game da abubuwan da ke faruwa a Lebanon, ta rubuta: "Abin da muke gani a yau a kudancin Lebanon yana haifar da shakku mai tsanani game da makomar tsarin kasa da kasa".
Jaridar ta ishara da cewa, ba za a iya ɗaukar fadada ayyukan soji na gwamnatin yahudawa a cikin ƙasar Lebanon da nufin samun iko akan wurare masu mahimmanci a kudancin wannan ƙasa a matsayin "yanayin tsaro na wucin gadi" ba, sai dai dole ne a dauke shi a matsayin wani lamari na siyasa mai girma da ke da alaƙa da ra'ayin ikon kasa da 'yancin ƙasashe na gudanar da ƙasashensu ba tare da matsin soji ba.
A cewar jaridar, ƙimar ƙasashe ba a auna su ne kawai da ikonsu na kare iyakokinsu ba, sai dai a girman da al'ummar duniya ke girmama waɗannan iyakoki da kuma barin ƙarfin soji ya zama hanyar tilasta sabbin abubuwan da suka faru.
Jaridar ta yi imanin cewa, hadarin abubuwan da ke faruwa a Lebanon ya kun shi: mamayewar soji tsakanin ƙasashe ba wai kawai yana shafar ɓangarorin da ke rikici ba ne, sai ma yana shafar ƙa'idodin da ke tsara dangantakar kasa da kasa. Rashin daukar mataki kan ikon ƙasashe yana buɗe hanya ga rikice-rikice masu yawa, kuma yana raunana amincewa ga tsarin shari'a na kasa da kasa wanda aka kafa don hana rikice-rikice da hana tilasta ra'ayi ta hanyar makami.
"Ar-Riyadh" ta jaddada cewa batun Lebanon ba wai kawai batun cikin gida ko yanki ba ne, ta bayyana cewa waɗannan abubuwan da ke faruwa wani bangare ne na wata muhawara ta kasa da kasa mai faɗi game da makomar tsaro da kwanciyar hankali a cikin duniyar da matsaloli da rikice-rikice ke ƙaruwa a cikinta.
…………………………………
Your Comment