Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (ABNA) ya habarta cewa: Kungiyar Fursunoni ta Falasdinawa ta sanar a cikin sabon rahotonta na Afrilu 2026 cewa gwamnatin Isra'ila tana tsare da mata Falasdinawa sama da 700 tun lokacin da aka fara yakin a ranar 7 ga Oktoba, 2023. Adadin matan da aka tsare a cibiyoyin tsare mutanen Isra'ila, musamman a gidan yarin Damon, ya karu kuma ya kai kimanin 90 a watan Afrilun 2026. Rahoton ya yi ishara da shari'o'i da dama na take hakkin dan adam ga fursunonin mata. A cewar kungiyar Fursunoni ta Falasdinawa, wadannan matan suna fuskantar munanan yanayi kamar duka, bincike mai wulakanci, cin zarafin mata, da barazanar kisa.
Isra'ila ta tsare matan Falasdinawa sama da 700 wanda suke fuskantar munanan yanayi kamar duka, bincike mai wulakanci, cin zarafin mata, da barazanar kisa.
Your Comment