ABNA24 : Shugaban hukumar zaben kasar ta Aljeriya da ta shirya kada kuri’ar raba gardamar, Muhammad Sharafi ya bayyana cewa; adadin wadanda su ka kada kuri’ar bai wuce kaso 23. 7 % ba, da hakan yake nufin mutane miliyan 5.5 daga tsakanin mutane miliyan 32.5 da su ka cancanci kada kuria.
A yayin zaben shugaban kasar da aka gudanar a watan Disamba na 2019 da ya dora shugaba Tabun akan mulki wadanda su ka kada kuri’ar sun kai kaso 39.93, wacce a wancan lokacin ma aka dauke ta mafi rauni.
An kada kuri’ar ne dai adaidai lokacin da shugaban kasar ta Aljeriya Tabun yake jiyya a kasar Jamus.
342/