26 Disamba 2021 - 18:08
Shugaban Kungiyar Kasashen Larabawa Ya Aikawa 'Yan Siyasar Libiya Wasika

Shugaban kungiyar kasashen Larabawa wanda yake birnin Alkahira na kasar Masar ya aikawa shugabannin kasar Libya yaso bayan da suke dage zaman shugaban kasa wanda yakamata a gudanar a cikin wannan wato zuwa wani lokacin da basu bayyana ba.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - A cikin sakon dai Ahmed Aboul Gheit yay i kira ga shuwagabannin kasar su dubi al-ummar kasarsu da kuma matsalolin da suke ciki, kada su biyewa son zuciyarsu, su gaggauta gudanar da zabubbuka a kasar wanda zai taimaka wajen dawo da zaman lafiya mai dorewa a kasar.

Daga karshe Ahmed Aboul Gheit ya kirayi ‘yan siyasar kasar su warware matsalolin da ke tsakaninsu a cikin ruwan sanya ta hanyar tattaunawa, kada su dauki makamai don wani sabani da ya bullo tsakaninsu.

342/