8 Satumba 2021 - 13:45
Palestine: Jihadul Islami Ta Gargadi Isra’ia Game Da Kai Hari A Yankin Jinin

Rahotanni da suke fitowa daga yankin palasdinu sun nuna cwa kungiyar gwagwarmayar yanto yankin na paladinu ta Jihadil Islami ta aike da dakarunta domin kasancewa cikin shirin ko ta kwana adaidai lokacin da ake tsammanin sojojin HKI za su kai hare - hare,

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {A.S} - ABNA : Sojojin HKI sun kai wani samame na kokarin kama fursunoni falasdinawa guda 6 da suka tsere daga gidan yarin Gilboa a ranar litinin da ta gabata, duk da tsananin tsaro da ake bawa gidan yarin, wanda ake daukar sa a matsayin gidan yari mafi tsaro a Isra’ila

A wani taron manema labarai da kungiyar ta Jihadil islami ta kira ta fadi cewa Idan sojojin Isra’ila suka kuskura suka shiga birnin Jenin to za su fuskanci turjiya da karfin manyan makamai , kuma ta ce za ta mayar da martani mai zafi idan aka samu wani canji kan Fursunoni palasdinawa da ke gidan Yarin Isra’ila domin jikkata duk wani bafalasdine guda daya jan layi ne gareta.

342/