kamfanin dillancin labaran ABNA ya habarta cewa, shafin yada labarai na Aljazeera ya bayar da rahoton cewa, an kai wa wata dalibar makarantar sakandire ta John Rostan hari a birnin Cannes da ke arewa maso yammacin Faransa ta hanyar jefa gyalenta a cikin kwandon shara tare da yayyaga kwafin alqur'ani da ke hannunta.
A cewar jami'an makarantar, wannan daliba ‘yar kasar Faransa mai hijabi ta gamu da firgici da tashin hankali bayan wannan harin.
Shugaban makarantar Sébastien Duval Rocher ya bayyana wannan mataki a matsayin wani lamari mai hatsarin gaske a makarantar da ke karkashinsa, shugaban makarantar, Sébastien Duval Rocher, ya fitar da sako ga daliban yayin da yake yin Allah wadai da wannan harin na kyamar Musulunci, yana mai cewa: “Makarantarmu a ko da yaushe tana karfafa bambancin ra’ayi da hakuri da al’adu, dukaknin addinai an yarda da su a wannan makaranta ba tare da nuna banbanci ba.
Dangane da haka ne kungiyar hadin gwiwar yaki da kyamar addinin Islama a kasar Faransa ta yabawa shugaban wannan makaranta da yayi Allah wadai da faruwar lamarin tare da neman ya dauki matakin hana afkuwar irin wannan lamari a nan gaba.
Har ila yau, wasu masu fafutuka na musulmin kasar Faransa sun sanar a shafukan sada zumunta cewa: Wannan lamari na daga cikin mummunan tasirin takunkumin da aka kakaba wa dalibai musulmi a fadin kasar, kuma karuwar kyamar musulmi a kasar Faransa ya mayar da wannan kasa, kasar takurawa musulmi.
342/