Kafar watsa labaran Tasnim ta Iran ta ba da labarin cewa a wata sanarwar da ta fitar a daren jiya Litinin, ma'aikatar harkokin wajen kasar Rashan ta bayyana haramtacciyar kasar Isra'ila a matsayin ummul aba'isin kara dagula lamurran tsaro a Zirin Gazan da ke karkashin killacewar HKI.
Wannan sanarwar ta ma'aikatar harkokin wajen Rashan ta biyo bayan rikicin da ya barke ne a kan iyakan Zirin na Gaza da yankunan da yahudawan suka mamaye sakamakon wasu hare-hare da suka kai Zirin na Gaza.
Shi ma a nasa bangaren babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya, António Guterres, ya bayyana cewa sake kaddamar da yaki a Gaza din zai zamanto mai tsanani kuma zai haifar da gagarumin rikici a yankin.
................
300