28 Mayu 2026 - 11:43
Source: ABNA24
Amurka Ta Kai Hari A Wuraren Soji A Birnin Bandar Abbas

Rundunar tsaron sararin samaniya ta birnin Bandar Abbas kaitsaye bayan harin ta fara aiki domin fuskantar maƙiyan da ke kai hari.

Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (AS) – ABNA - ya habarta cewa: Da sanyin safiyar yau Alhamis, mazauna yankin sun ba da rahoton jin karar fashewa a birnin Bandar Abbas.

Bisa ga wannan rahoto, ba a san ainihin dalilin wannan karar ba, kuma har yanzu babu wata cibiya a hukumance da ta bayyana ra'ayinta game da dalilin faruwar wadannan kararraki. Wasu rahotanni sun nuna cewa, rundunar tsaron sararin samaniya ta birnin Bandar Abbas ta fara aiki a cikin 'yan mintuna domin fuskantar makaman da ke kai hari.

Wani jami'in Amurka a cikin tattaunawa da kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ce, sojojin Amurka sun harbo jiragen Iran marasa matuki waɗanda ke barazana ga sojojin Amurka da zirga-zirgar jiragen ruwa na kasuwanci a hanyoyin teku. Wannan jami'in ya kara da cewa: Sojojin Amurka sun kai sabbin hare-hare a kan wani wurin soji na Iran, wanda wannan wurin ya kasance barazana ga sojojin Amurka da tsaron zirga-zirgar jiragen ruwa a mashigar Hurmuz.

Your Comment

You are replying to: .
captcha