21 Mayu 2026 - 00:25
Source: ABNA24
Iran Ta Yi Barazanar Yanke Igiyoyin Intanet Da Ke Ƙarƙashin Teku A Mashigar Hormuz

Iran ta ba wa manyan kamfanonin fasaha na duniya wa'adi don su amince da dokokin Tehran kuma su biya kudin wucewa ga igiyoyin Intanet na ƙarƙashin teku da ke wucewa ta mashigar Hormuz. 

Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (ABNA) ya habarta cewa: A cewar wannan kafofin watsa labarai, Iran na neman cikakken ikon gyara da kula da waɗannan igiyoyin, kuma ta yi barazanar cewa rashin bin umarnin kamfanoni na iya haifar da yanke waɗannan hanyoyin sadarwa.

Wannan jaridar ta Sahayoniya, tana nuna fargabar ikon sojin Iran, inda ta yi gargaɗi cewa lalacewar waɗannan igiyoyin ta hanyar jiragen ruwa marasa matuka da kananan jiragen ruwa na karkashin teku na Iran, zai gurgunta tsarin banki na duniya, sadarwar soja, da abubuwan more rayuwa na basirar wucin gadi (AI) a duk faɗin duniya; abin da aka ambata a matsayin "bala'i na dijital" ga dukkan nahiyoyi.

Your Comment

You are replying to: .
captcha