Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (ABNA) ya ruwaito cewa: Bayan da Trump yayi tir da rashin hadin gwiwar kasashen NATO da Turai kan yakar Iran, amma sai ga UAE, Qatar da Saudi Arabia sun goya masa baya inda suka kai hari a cibiyar tace mai ta Pars Petrochemical da ke Kudancin Pars Assaloyeh da ke Bushehr sun kai hari kan ɓangaren daban-daban na cibiyar. Har yanzu ba a tantance ainihin bayanan sakamakon harin ba.
Amma Rahotanni daga kafafen yada labarai sun ce, bayan wannan harin Iran ta harba makamai masu linzami 13 da wasu jirage marasa matuka 27 na kunar bakin wake a sansanin Amurka da ke Hadaddiyar Daular Larabawa.
Ra'ayinka