Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (ABNA) ya ruwaito cewa: Iran ta ki hari mai tsanani da jiragen marasa matuka na sojojinta kan matattarar jiragen yakin Isra’ila da jiragen tankokin dakon man fetur da suke a filin jirgin saman Ben Gurion wanda wadannan jirage suna taka muhimmiyar rawa wajen kai harin ta'addanci a kan kasar Iran da fagen gwagwarmaya.
Ofishin hulda da jama'a ta rundunar ta sanar a cikin sanarwar mai lamba 33: Tun daga safiyar yau, a ayyukan ramuwar gayya ga tsarkakakken jinin jaruman shahidai na jirgin Dena da jinin Dakta Ali Larijani da Manjo Janar Gholamreza Soleimani, mun gudanar da kai da hare-hare jirage marasa matuki kan wurin da jiragen saman gwamnatin Sahayoniyya ke jibge a filin jirgin saman Ben Gurion.
A cikin wannan sanarwar, sojojin Jamhuriyar Musulunci ta Iran, yayin da suke yabawa da jinjinawa bisa halartar yawan jama'a cikin jarumta a taron bankwana da shahidan Dena, sun kira wannan halartar da hadin kai da yake a matsayin ginshiki na karfafa ruhin sojojin tare da jaddada cewa: Zasu ci gaba da ayyukan ramuwar gayya ga abokan gaba na Amurka da Isra’ila da dukkan iyawarsu.
Jiragen yakin sojojin saman Isra'ila da tankokin dakon mai da suke jibge a filin jirgin saman Ben Gurion sun taka muhimmiyar rawa wajen ta'addanci kai tsaye da tallafawa hare-haren jiragen sama a kan kasar Iran da fagen gwagwarmaya.
....................................
Ra'ayinka