Yamen: Ta Kai Hari Kan Jirgin Ruwan Minervagracht A Mashigin Tekun Aden

Sojojin Yaman sun harbi jirgin ruwan Minervagracht da makami mai linzami a mashigin tekun Aden
1 Oktoba 2025 - 11:15
Source: ABNA24
Yamen: Ta Kai Hari Kan Jirgin Ruwan Minervagracht A Mashigin Tekun Aden

A cikin wata sanarwa da rundunar sojin kasar ta fitar ta tabbatar da cewa sojojin ruwan sun kai wani harin soji kan jirgin ruwan Minervagracht saboda kamfanin jrigin ya keta dokar hana shiga tashar jiragen ruwa na Falasdinawa.

Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na na Ahlul Baiti (AS) – ABNA– ya habarto cewa: A yau ne sojojin kasar suka sanar da cewa an harbawa jirgin ruwan Minervagracht makami mai linzami a mashigin tekun Aden. A cikin wata sanarwa da rundunar sojin kasar ta fitar ta tabbatar da cewa sojojin ruwan sun kai wani harin soji kan jirgin ruwan Minervagracht saboda kamfanin jrigin ya keta dokar hana shiga tashar jiragen ruwa na Falasdinawa.

Sanarwar ta bayyana cewa an kai harin ne a mashigin tekun Aden da makami mai linzami. Aikin dai ya yi sanadin samun jirgin kai tsaye, lamarin da ya sa ya kama shi wuta. A halin yanzu yana cikin hadarin nutsewa.

Rundunar sojin kasar ta bayyana cewa, wannan martani ya zo ne a cikin tsarin kare al'ummar Palastinu da ake zalunta da kuma Mujahidansu, da mayar da martani kan laifukan kisan kiyashi da yunwatarwa da makiya yahudawan sahyoniya suke aikatawa kan 'yan'uwanmu a zirin Gaza, tare da tabbatar da ci gaba da haramta zirga-zirgar jiragen ruwa ga makiya Isra'ila a tekun Bahru maliya da na Larabawa.

Dakarun sun nanata cewa al’ummarmu masu girma, masu hakuri, mujahiddanmu za su ci gaba da ba da goyon baya da kuma kare al'ummar Palastinu da ake zalunta daga aikata laifukan ta’addancin karni. Sun kara da cewa ana ci gaba da gudanar da ayyukan soji kuma ba za su gushe ba har sai an daina kai hare-hare tare da dage kawanyar da aka yi a zirin Gaza.

Rundunar sojin ta kuma tabbatar da ci gaba da aiwatar da dokar haramta haramtacciyar kasar Isra'ila a Bahru maliya da na Larabawa, Babal-Mandab, da mashigin tekun Aden, tare da jaddada gargadin su ga daukacin kamfanoni da jiragen ruwa a kan keta dokar haramcin da aka sanar a baya.

Hukumar kula da kasuwanci ta ruwa ta Birtaniya UKMTO ta sanar a ranar Litinin cewa an kai hari kan wani jirgin ruwa a mashigin tekun Aden mai nisan kilomita 128 kudu maso gabashin Aden. Kyaftin din jirgin ya ba da rahoton "ganin wani karo a saman ruwa da hayaki yana tashi a sararin sama a bayan jirgin".

Your Comment

You are replying to: .
captcha