2 Oktoba 2024 - 11:04
Ana Ci Gaba Da Fafatawa A Fagen Daga Tsakanin Mayakan Hizbullah Da Sojojin Yahudawan Sahyoniya

Kungiyar Hizbullah ta kara da cewa: A cikin wannan rikici an raunata dimbin sojojin yahudawan sahyoniya kuma har yanzu ana ci gaba da gwabzawa.

Kungiyar Hizbullah ta kasar Labanon ta sanar a yau Laraba cewa: Mayakan gwagwarmayar Islama na kasar Labanon suna fafatawa da sojojin yahudawan sahyoniyawan da suka kutsa kai garin Maroon al-Ras da ke kan iyakar kasar ta Lebanon daga gabas.

Kungiyar Hizbullah ta kara da cewa: A cikin wannan rikici an raunata dimbin sojojin yahudawan sahyoniya kuma har yanzu ana ci gaba da gwabzawa.