Har ila yau, an bayar da rahoton
cewa, an samu nasarar harin da dakarun Hizbullah na kwanton bauna a garin
Al-Adisah inda harin ya hada sosjojin Komando 20, inda aka aike da jirage masu
saukar ungulu 4 na Isra'ila domin jigilar wadanda suka jikkata da kuma wadanda
suka mutu.
Kafofin yada labaran yahudawan sahyuniya sun tabbatar da cewa an kashe sojoji 4 tare da raunata 20 a harin kwantan bauna da kungiyar Hizbullah ta kai a garin Al-Adisa.
Mutane 15 ne suka mutu da jikkatar wasu sakamakon harin kunar bakin wake da aka kai kan Sahayoniyawa Sojojin Isra'ila da suka ji rauni ya tsananta a harbin Tel Aviv
Akalla yahudawan sahyuniya 7 ne suka mutu inda wasu 8 suka samu raunuka sakamakon harbin da aka kai a birnin Jaffa na Tel Aviv wanda bai samu kulawa da daukar hankali ba sosai ba sakamakon harin na Iran mai Taken Tabbatacen Alkawari Na 2.
A cewar rahotanni da aka buga, mutane biyu daya dauke da makami daya kuma dauke da wuka, sun kai wani samame a Tel Aviv.
Sojojin yahudawan sahyoniya sun tabbbatar da cewa wata mace sojan sahyoniyawan ta samu munanan raunuka a wannan farmakin kuma halin da take ciki na cikin mawuyacin hali.