Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - Jaridar leadership ta Najeriya ta nakalto mai bawa shugaban majalisar shawara kan al-amuran watsa labarai Ola Awoniya yana fadar haka a jiya Asabar a wata sanarwa da ya fitar.
Labarin ya kara da cewa shugaban majalisar dattawan ya bukaci a warware matsalar da ke faruwa tsakanin kungiyar ASSU ta malaman makaranta da kuma gwamnatin tarayyar don a samu a sake bude jami’o’in kasar da gaggawa.
Kungiyar ASSU ta malaman jami’o’I a Najeriya suna yajin aikin kimani watanni biyu kenan, saboda rashin cika alkawarin da gwamnatin tarayya kasar ta yi masu a shekarun da suka gabata, na hakkokinsu da kuma kyautata yanayin karatu a jami’I’o’in kasar.
342/