26 Mayu 2017 - 10:18
Iran: Za A Fara Neman Ganin Jaririn Wata Ramadan Da Yammacin Yau Juma'a

Shugaban cibiyar neman jaririn watan a gundumar Yazd ya sanar da tura kungiyoyin kwararru hudu zuwa sassan daban-daban na gundumar domin ganin jaririn watan.

Shugaban cibiyar neman jaririn watan a gundumar Yazd ya sanar da tura kungiyoyin kwararru hudu zuwa sassan daban-daban na gundumar domin ganin jaririn watan.

A yau juma'a ne Hujjatul-Islam Ali Ridha Sharifi ya fadawa kamfanin dillancin labarun Irna cewa; A cikin wadannan gungu-gungu na mutane,da akwai kwararru 20 da su ka hada masana ilimin falaki.

Mutanen za su zauna a kauyukan Ardkan, Mubid, da kuma wani sashe na kauyen Taft domin sa ido akan fitowar jaririn watan gabanin faduwar ranar yau juma'a.

Sharifi ya ci gaba da cewa; Saboda ba abu ne mai yiyuwa  ba a iya ganin jaririn watan kai tsaye da idanu a gundumar ta Yazd, kungiyoyin za su yi amfani da na'urorin zamani na hangen nesa.

Kungiyoyin da su ke aiki a gundumar ta Yazd, suna a karkashin  cibiyar ganin watan azumi ne ta kasa.288