Kamfanin dillancin labarai na Ahlul Bait (AS) - ABNA - ya ruwaito cewa: Hukumar Shari'a ta bayyana cewa: An rataye Mojtaba Kiyan Muhammadqoli, wanda yake ɗaya daga cikin ma'aikatan Amurka da Isra’ila, wanda a lokacin yakin da aka yi a baya-bayan nan ya aika bayanai game da sassan masana'antar tsaron ƙasar ga makiya, bayan gabatar da ƙarar da kuma gudanar da shari'a a kotun lardin Alborz, da safiyar yau Litinin, 3 ga watan Khordad, wanda yayi daidai da 24/04/2026 bayan da Kotun Ƙoli ta amince da hukuncin da kuma bin hanyoyin doka, an rataye shi.
Bisa binciken da aka yi, wanda aka ambata a lokacin yakin da aka yi a baya-bayan nan ya aika saƙonni da yawa zuwa cibiyoyi masu alaƙa da makiya na Amurka da Isra’ila, wanda daga cikinsu akwai taswirori da bayanan wuraren samar da sassa masu alaƙa da masana'antar tsaron ƙasar.
Wanda aka yanke wa hukuncin a cikin yanayin yaƙi, a cikin saƙonnin da ya aika zuwa cibiyar da ke da alaƙa da makiya, ya aika bayanan wuraren kamfani masu alaƙa da masana'antar tsaro, kuma ya ambaci sunan firaministan gwamnatin yahudawa a cikin saƙon da ya aika ga jami'an wannan cibiyar yana mai jaddadawa cewa su "ba wa BB (Bibi Netanyahu) labari".
Mojtaba Kiyan a cikin furucinsa ya ce: "Bayan na aika saƙo zuwa gidan talabijin na tauraron dan adam, sun ba ni lamba don in aika bayanan, ni kuma na aika bayanan ta wannan hanyar".
Binciken fasaha na saƙonnin da aka yi musayar tsakanin wanda aka yanke wa hukunci da makiya ya nuna cewa kwanaki 3 bayan aika bayanan, wurin da aka nuna ya zama hadafin hari daga makiya kuma sun lalata shi gaba ɗaya.
Bayan da Mojtaba Kiyan ya tuntuɓi cibiyar yada labarai ta makiya, an gano shi nan take kuma aka kama shi. An gudanar da shari'ar Mojtaba Kiyan a kotun lardin Alborz tare da bin ka'idodin doka da kuma halartar lauyansa.
Bayan an yi shari'ar, bisa la'akari da hujjoji da yawa ciki har da furucin da wanda ake tuhuma ya yi a gaban mai shari'a da kuma a kotu, da gano wayarsa da lambar wayarsa wadda ta aikewa da saƙonni guda takwas, ciki har da saƙonnin game da bayanan wuraren samar da masana'antar tsaron ƙasar, zuwa cibiyar makiya, tare da masaniyar wanda ake tuhuma yake da shi game da ayyukansa da kuma cikakken saninsa game da yanayin cibiyar makiya da ya aika saƙonnin da ke ɗauke da bayanan, kotu ta yanke wa Mojtaba Kiyan hukuncin kisa da kuma kwace dukiyoyinsa bisa ga sashi na ɗaya na dokar tsaurara hukuncin leƙen asiri da haɗin kai da gwamnatin yahudawa da ƙasashen da ke yaƙi da tsaro da muradun ƙasa, saboda zargin aikata ayyukan leƙen asiri ga gwamnatin yahudawa da Amurka.
Da wanda ake tuhuma ya yi ƙara, an mika ƙarar zuwa Kotun Ƙoli inda aka yi nazari a kanta, kuma bisa ga takardu da shaidun da ke cikin ƙarar, bayan kin amincewa da ƙarar, an amince da hukuncin.
An zartar da hukuncin ne bayan an gama bin ka'idojin doka, da safiyar yau Litinin, 3 ga watan Khordad, kuma aka rataye Mojtaba Kiyan.
Bisa ga wannan rahoto, tare da umarnin na musamman na shugaban hukumar shari'a na gudanar da shari'a mai tsauri da gaggawa a kan shari'o'in masu cin amanar ƙasar da suka yi haɗin gwiwa da makiya Amurka da yahudawa ta kowace hanya, an kuma gama wannan shari'a a kotun lardin Alborz cikin kankanin lokaci tare da bin ka'idojin doka, ta yadda daga lokacin da aka kama wanda ake tuhuma har zuwa lokacin da aka zartar da hukuncin a ranar 3 ga Khordad, 1405 bai wuce kwanaki 5 ba.
Your Comment