23 Mayu 2026 - 18:58
Source: ABNA24
Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Aike Da Muhimmin Saƙo Ga Shugaban Hizbullah

Araghchi: Iran Ba Za Ta Daina Goyon Bayan Hizbullah Ba

Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (ABNA) ya habarta cewa: Sayyid Abbas Araghchi, ministan harkokin wajen ƙasar iran, a cikin saƙonsa ga Sheikh Naim Qassem, shugaban ƙoli na Hizbullah, ya tabbatar da cewa Jamhuriyar Musulunci ba za ta daina tallafawa ƙungiyoyin da ke neman hakki da 'yanci ba har zuwa lokaci na ƙarshe, kuma Hizbullah mai juriya da nasara tana kan gaban waɗannan ƙungiyoyi ɗin.

Araghchi ya kara da cewa, tun daga farko lokacin da wasu ƙasashen yankin suka shiga tsakani don rage tashin hankali tsakanin Iran da Amurka, Iran ta sanya alakar tsagaita wuta a Lebanon da duk wata yarjejeniya a matsayin sharadi, kuma wannan ƙa'ida ta kasance ba abar da za'ai shakka ba ce har zuwa yanzu, kuma tana cikin buƙatun haƙƙin gwamnati da al'ummar Iran, kuma za ta kasance akan hakan.

Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa, a cikin shawarwarin karshe da Jamhuriyar Musulunci da ta gabatar ta hanyar mai shiga tsakani na Pakistan don dakatar da yaƙi na dindindin, an sake nanata cewa dole ne a sanya Lebanon a cikin yarjejeniyar tsagaita wuta.

....................

Your Comment

You are replying to: .
captcha