8 Mayu 2026 - 17:48
Source: ABNA24
A Harin Da Amurka Ta Kai Kan Jirgin Fasinjar Iran 1 Yayi Shahada 10 Sun Ji Ciwo 4 Sun Bace

A daren jiya (Alhamis, 7 ga Mayu), jirgin ruwan fasinja (leng) mallakin mutanen yankin Kolahi na Minoab, a cikin tekun Hormuz da Makran (Oman), ya fuskanci harin sojojin Amurka. Wannan harin ya haifar da gobara a jirgin.

Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (ABNA): Adadin wadanda suka jikkata da kuma wadanda aka bace Gwamnan Minoab, Mohammad Radmehr, ya bayyana cewa: Mutane 15 ne suke cikin jirgin. 10 daga cikinsu sun jikkata kuma ana kwantar da su asibiti. 5 sun bace, ana ci gaba da neman su da taimakon jama'a da ƙungiyoyin bincike. Daga baya aka samu gawar 1 daga cikin wadanda suka bace, wanda hakan ya rage adadin waɗanda ake nema zuwa 4.

Martanin Iran

A cewar rahotanni, sojojin Iran sun mayar da martani nan take. Sun kai hari kan jiragen ruwan yakin Amurka da ke gabashin tekun Hormuz da kudancin tashar jiragen ruwa ta Chabahar, inda suka yi musu barna mai yawa.

Your Comment

You are replying to: .
captcha