13 Nuwamba 2025 - 10:17
Source: ABNA24
WFP Ta Bukaci Karin Taimako Ga Gaza A Yayin Da Isra’ila Ke Cigaba Da Keta Dokar Tsagaita Wuta

Shirin Abinci na Duniya na Majalisar Dinkin Duniya ya yi kira da a kara tallafin jin kai ga Gaza da kuma kare yarjejeniyar tsagaita wuta. A watan Oktoba, mutane 200,000 sun sami tallafin kudi na dijital wanda da sune mutane miliyan daya suka sami tallafin abinci. Duk da yarjejeniyar tsagaita wuta amma ci gaba da take hakkin Falasdinawa da Isra'ila ke ci gaba da yi na kawo cikas ga kokarin murmurewa.

Kamfanin dillancin labaran kasa da kasa na AhlulBaiti (As) –ABNA-ya habarta cewa: Shirin Abinci na Duniya na Majalisar Dinkin Duniya (WFP) a ranar Laraba ya jaddada bukatar gaggawa ta fadada isar da kayan agaji ga yankin Gaza da kuma tabbatar da dorewar yarjejeniyar tsagaita wuta.

A cikin rubuce-rubuce guda biyu daban-daban a dandalin sada zumunta "X," hukumar Majalisar Dinkin Duniya ta ruwaito cewa kusan mutane 200,000 a Gaza sun sami tallafin kudi na dijital na gaggawa a watan Oktoba.

WFP ta bayyana cewa wannan tallafin kudi ya bai wa iyalai damar siyan abinci da muhimman abubuwa daga kasuwannin gida, ta kara da cewa adadin ya kai kashi 100% na burin da hukumar ke son cimmawa a kowane wata.

Kungiyar ta kuma lura cewa mutane miliyan daya a Gaza sun sami tallafin abinci daga WFP, amma ta jaddada cewa "murmurewa zata kasance mai tsawo lokaci".

“Bayan wata guda da tsagaita wuta,” in ji WFP, “iyalai a Gaza suna ci gaba da fafutukar sake gina rayuwarsu.”

An aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza a ranar 10 ga Oktoba bayan shekaru biyu na zaluncin Isra'ila. Duk da haka, sojojin Isra'ila suna ci gaba da karya yarjejeniyar tsagaita wuta kowace rana tare da hana shigar da mafi yawan kayan agajin jin kai cikin yankin da aka kewaye.

Your Comment

You are replying to: .
captcha