13 Afirilu 2025 - 11:16
Source: Irna
MDD: Sama Da 100 Ne Aka Kashe A Harin Da Aka Kai A Sansanonin Yankin Darfur Na Kasar Sudan

Wani jami'in Majalisar Dinkin Duniya ya ce sama da mutane 100 da suka hada da yara 20 ne aka kashe a wani hari da aka kai kan sansanonin 'yan gudun hijira a yankin Darfur na kasar Sudan.

Wani jami'in Majalisar Dinkin Duniya ya sanar a jiya Asabar cewa, wata kungiyar 'yan tawayen kasar Sudan ta kaddamar da wani farmaki na kwanaki biyu kan sansanonin 'yan gudun hijira da ke fama da yunwa a yankin Darfur, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutane fiye da 100 da suka hada da yara 20 da ma'aikatan agaji 9.

Clementine Nkota Salami, jami’in kula da ayyukan jin kai na Majalisar Dinkin Duniya a Sudan, ya bayyana cewa, dakarun gaggawa da mayakan sa-kai sun kaddamar da farmaki kan sansanonin Zamzam da Abu Shorouk da kuma garin El Fasher da ke kusa, babban birnin lardin Darfur a ranar Juma’a.

Al-Fasher dai na karkashin rundunar soji ne, wanda ke fafatawa da dakarun sakai tun bayan da Sudan ta fada yakin basasa shekaru biyu da suka gabata, wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane sama da 24,000, ko da yake masu fafutuka sun ce adadin ya zarta haka.

A wata sanarwa da Nekota Salami ya fitar ta ce an sake kai wa sansanonin hari a ranar Asabar. Ya ce an kashe ma'aikatan agaji tara a lokacin da suke halartar daya daga cikin 'yan tsirarun cibiyoyin kiwon lafiya da suka rage a sansanin Zamzam".

Ya kara da cewa "Wannan wani mummunan tashin hankali ne da ba za a amince da shi ba a cikin jerin munanan hare-haren da aka kai kan mutanen da suka rasa matsugunansu da ma'aikatan agaji a Sudan tun bayan barkewar rikici kusan shekaru biyu da suka wuce".

Yakin basasar Sudan ya fara ne a watan Afrilun shekarar 2023 tare da kara tsamarin fadace-fadace tsakanin sojojin Sudan da dakarun "Rapid Support Forces" karkashin jagorancin "Mohammed Hamdan Daqlou", wanda aka fi sani da "Hamidati", da kuma shiga tsakani na kasa da kasa don kawo karshensa ya ci tura.

Rahotanni sun ce yakin na Sudan ya zarce kan iyakokinsa na farko, sannan kuma ya hada da kasashen Chadi da Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya.

A farkon watan Disambar shekarar da ta gabata ne gwamnatin Abdel Fattah al-Burhan a Sudan ya zargi kasar Chadi da kyale jiragen yakin saman Emiratesu tashi daga yankin Chadi zuwa Sudan.

Rundunar sojin Sudan ta sanar da cewa, "Njamnaa" (chadi) ta shiga tsakani kai tsaye a yakin basasar Sudan, musamman a yankin Darfur, kan sojojin Sudan, ta hanyar kawance da Hadaddiyar Daular Larabawa.

A watan Janairun da ya gabata ne Amurka ta sanar da kakaba takunkumi kan Hamidati, shugaban kungiyar Rapid Support Forces (RSF) da wasu dillalan makamai na Masarautar, bayan da ta bayyana cewa dakarun gaggawa na RSF da mayakan sa-kai a yankin Darfur na kudancin Sudan sun aikata kisan kiyashi.

Your Comment

You are replying to: .
captcha