12 Satumba 2024 - 05:57
Sheikh Ibrahim Ya'aqub Alzakzaky Ya Taya Al'ummar Barno Jimamin Ibtila'in Ambaliyar Ruwa Da Ta Same Su + Hotuna

Wannan shine matanin rubutun da aka fitar daga ofishin babban malamin kuma shugaban harkar musulunci a Nigeria Sheikh Ibrahim Ya'aqub Alzakzaky Hf

Wannan shine matanin rubutun da aka fitar daga ofishin babban malamin kuma shugaban harkar musulunci a Nigeria Sheikh Ibrahim Ya'aqub Alzakzaky Hf 

بسم الله الرحمن الرحیم 

Da sunan Allah, Mai Rahama, Mai Jin Ƙai 

إنا لله وإنا إليه راجعون

Sakamakon mummunar ambaliyar ruwa da ke aukuwa a Jihar Borno, wanda ya yi sanadiyar rashin rayuka da jikkata jama'a masu yawa, tare da hasarar dukiyoyi da dama, Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) na jajanta ma iyalan dukkan waɗanda wannan bala'i ya shafa. Ya yi kira ga hukumomi da su ɗauki duk matakan da suka dace don gyara barnar da aka samu.

Jagora (H) ya roƙi Allah Maɗaukakin Sarki Ya jiƙan waɗanda suka rasu, Ya kuma gaggauta samun sauƙi ga waɗanda suka jikkata.

08/RabiuAwwal/1446

11/09/2024

Ambaliyar Ruwan Borno

@Szakzakyoffice