28 Afirilu 2026 - 10:41
Source: ABNA24
Hizbullah Ta Gudanar Da Ayyuka Guda 4 Kan Sojojin Isra’ila + Bidiyo

Lalle ne Ƙungiyar gwagwarmaya ta Musulunci ta himmatu wajen kare ƙasarta da jama'arta, musamman ganin yadda makiya Isra’ila suka wuce gona da iri ta hanyar aikata laifuka a kan iyakoki. Kuma wannan shi ne mafi ƙarancin abin da ya wajaba don hana su su ci gaba da mugayen manufofinsu da ke barazana ga Lebanon a matsayinta na ƙasa, al'umma, da gwagwarmaya.

Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (ABNA) ya habarta cewa: Domin kare ƙasar Lebanon da al’ummarta, da kuma mayar da martani ga keta yarjejeniyar tsagaita wuta da makiya Isra’ila suka yi, da cin zarafin fararen hula da lalata gidajensu da ƙauyukansu a kudancin Lebanon, da kuma dogaro da ‘yancin yin gwagwarmaya da fatattakar mamaya, Ƙungiyar gwagwarmayar Musulunci (Hizbullah) a ranar Litinin 27 ga Afrilu, 2026, ta fitar da sanarwar soji guda uku kamar haka:

1- Da ƙarfe 13:30, a matsayin ramuwa ga rushe gidaje a ƙauyukan kudancin Lebanon, mujahidai na gwagwarmayar Musulunci sun kai hari kan wata babbar motar soji ta Isra’ila nau'in D9 a yayin da take rushe gidaje a cikin garin Bint Jbeil, bisa amfani da wani jirgin mara matuki kuma sun samu tabbataccen cimma hari.

2- Da ƙarfe 14:00, a matsayin ramuwa ga hare-haren da aka kai wa ƙauyuka da rushe gidaje a kudancin Lebanon, mujahidai na gwagwarmayar Musulunci sun kai hari kan wata tankar Merkava a garin Qantara, ta amfani da jirgin mara matuki kuma sun samu tabbacin cimma hari.

3- Da ƙarfe 17:30, a matsayin ramuwa ga hare-haren da aka kai wa ƙauyuka a kudancin Lebanon wanda suka yi sanadiyar shahadar mutane da raunata fararen hula da dama, mujahidai na gwagwarmayar Musulunci sun kai hari kan tarin sojojin makiya Isra’ila guda biyu a garin Naqoura, ta amfani da jirage marasa matuki guda biyu, kuma sun samu tabbacin cimma hari raunata ko kashe sojojin.

Your Comment

You are replying to: .
captcha