Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (ABNA) ya ruwaito cewa: Jami’an Tsaron sarrain samaniyar Iran a Tehran suna ci gaba da fuskantar da aranagama da ba da kariya ga hare-hare masu ta’addancin Amurka da Sahyoniya tun bayan fara kai hare-haren da Amurka ta yi wa Iran.
A safiyar ranar Asabar, Amurka da Isra'ila sun kaddamar da hare-hare da dama a yankunan Tehran, biranen Isfahan, Qom da Kermanshah. Mintuna kadan bayan wannan tashin hankali, sojojin Iran sun fara kai hare-haren makamai masu linzami kan Isra'ila, inda suka kai hari kan Haifa, Tel Aviv, da wasu sansanonin sojin Amurka da ke yankin. Kwamandan hedikwatar "Khatam al-Anbiya" Manjo Janar Ali Abdullahi, ya ce masu ta’addancin su jira wani gagarumin martani mai tsauri da tsanani daga dakarun Jamhuriyar Musulunci ta Iran wanda suka gani somin tabi ne.
Your Comment