16 Yuli 2025 - 17:51
Source: ABNA24
Bidiyo | Na Yadda Isra'ila Ta Kai Hari Kan Ginin Ma'aikatar Tsaron Siriya A Damascus

Hare-haren sun nufaci ginin babban hafsan sojin kasar, da ma'aikatar tsaro da kuma kusa da fadar shugaban kasa.

Kamfanin dillancin labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Bait As -Abna- ya habarta cewa: jiragen yakin haramtacciyar kasar Isra'ila sun kaddamar da wani samame a birnin Damascus a ranar yau Larabar, inda suka nufaci ginin babban hafsan sojin kasar, da ma'aikatar tsaro da kuma kusa da fadar shugaban kasa.

A halin da ake ciki kuma ministan tsaron Isra'ila Yisrael Katz ya sanar da cewa an kawo karshen sakonnin gargadi ga Damascus tare da yin barazanar kai hare-hare masu zafi. Hakan ya biyo bayan sake barkewar rikici a Sweida da ke kudancin kasar.

Your Comment

You are replying to: .
captcha